![]() |
|
2019-08-11 15:49:11 cri |
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin madam Hua Chunying, ta bayyana cewa, a halin yanzu Hong Kong yanki ne na musamman dake karkashin ikon gwamnatin jamhuriyar jama'ar kasar Sin. Ta kara da cewa, lokaci ya riga ya wuce da yankin ya taba zama karkashin ikon Turawan mulkin mallaka na Birtaniya.
Kakakin ofishin ma'aikatar harkokin wajen Birtaniya ya ce, sakataren harkokin wajen kasar Raab, ya yi hira ta wayar tarho a ranar 9 ga watan Augasta da babbar jami'ar gudanarwar yankin Hong Kong, Carrie Lam, game da halin da ake ciki a yankin na Hong Kong.
A lokacin da aka nemi ya yi karin haske ta wayar tarho, Hua ta ce, Birtaniya ba ta da wani iko, ko 'yanci, ko kuma hakkin bibiyar al'amurran dake faruwa a yankin na Hong Kong. (Ahmad Fagam)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China