2019-07-15 10:13:03 cri |
An gaza gudanar da taron ne a karo na 2 saboda wakilan bangaren adawa ba su hallara ba.
Sai dai kwamitin mulkin sojin ko Tarayyar Afrika, ba su fitar da wata sanarwa dangane da dage tattaunawar ba.
Amma, Khalid Omer Yousif, jagora a kungiyar kawancen 'yan adawar, ya shaidawa manema labarai cewa, kungiyar ta nemi Tarayyar Afrika, daya daga cikin masu shiga tsakanin kan rikicin na Sudan, da ta jinkirta tattaunawar zuwa gobe Talata.
Tattaunawar da ake ta jinkirtawa na da nufin amincewa da kundin tsarin mulki wanda zai ba da iko ga masu mulkin rikon kwarya.
A ranar 5 ga watan nan ne kwamitin sojin da bangaren adawar, suka cimma yarjejeniyar kafa gwamnatin rikon kwarya da ta kunshi bangarorin biyu.
Bangarorin biyu sun amince da kafa majalisar mulki ta hanyar karba-karba a tsakaninsu na tsawon shekaru 3 da kuma gwamnatin farar hula mai cin gashin kanta. (Fa'iza Mustapha)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China