2019-07-13 16:49:11 cri |
Wakilin Tarayyar Afrika a Sudan, Mohamed Hacen Lebatt, ya ce bangarorin biyu sun gudanar da zagaye na 3 na tattaunawa karkashin kyakkyawan yanayi, kuma dukkansu sun amince da kunshin daftarin yarjejeniyar.
Bangarorin biyu sun kuma amince su gana a yau Aasbar, domin amincewa da daftari na 2, wanda ke kunshe da kundin tsarin mulki.
Wakilin Habasha Mahmud Dirir, ya shaidawa manema labarai cewa, abun da ya rage yanzu shi ne bayyana cimma yarjejeniyar a hukumance, wanda zai alamta shiga wa'adin mulkin rikon kwarya ko kuma sauyawar gwamnati zuwa ta farar hula. (Fa'iza Mustapha)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China