Ranar 28 ga watan Satumba, an rufe babban taro karo na 11 na kasashen da suka daddale yarjejeniyar hana kwararar hamada ta MDD a birnin Windhoek, hedkwatar kasar Namibia, wanda aka yi makonni 2 ana gudanarwa. Mahalarta taron sun cimma daidaito kan yadda za a kyautata aiwatar da yarjejeniyar yadda ya kamata, da cimma burin kasa da kasa na hana karuwar lalacewar yanayin kasa, da aka gabatar da shi a yayin taron koli na Rio +20 da aka yi a shekarar 2012.