"Akwai wasu bangarori dake neman hargitsa juyin juya halin kasar sakamakon irin nasarorin da aka cimma kawo yanzu, suna ci gaba da yunkuri wargaza yarjejeniyar da aka riga aka cimma domin jefa kasar cikin rudani," TMC ta bayyana hakan cikin wata sanarwa.
Wasu kungiyoyin da ba'a tantance su ba sun yi ta harba bindiga kan mai tsautsayi inda suka hargitsa yanayin tsaro a ciki da wajen inda masu zanga-zangar suke zaman dirshan," suna cin mutuncin fararen hula da dakarun sojojin dake bada kariya ga masu zanga-zangar," in ji sanarwar.
Majalisar sojojin ta sha alwashin yin aiki tare da bangarorin 'yan adawa na Freedom da Change Alliance domin daukar matakan shawo kan halin da ake fuskanta. (Ahmad Fagam)