Majalisar sojojin Sudan ta musanta yunkurin tarwatsa masu zaman dirshan a helkwatar sojojin
Majalisar sojoji mai shugabancin rikon kwarya a Sudan (TMC), ta sanar a ranar Lahadi cewa, ta musanta yunkurin tarwatsa dubban mutane masu zanga-zanga dake zaman dirshan a gaban babbar helkwatar sojojin kasar dake birnin Khartoum.
Majalisar sojojin, ta kuma gargadi wasu kungiyoyi, da su guji toshe manyan titunan mota a birnin Khartoum, TMC ta ce, wannan mataki ba za'a lamince shi ba saboda zai iya haifar da tashin hankali wanda ke bukatar hukumomi su dauki matakan da suka dace don shawo kan matsalar yadda ya kamata.(Ahmad Fagam)