in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalisar sojojin Sudan ta musanta kafa majalisar gudanar da mulkin kasar
2019-05-06 09:56:04 cri
Majalisar mika mulki ta dakarun sojojin Sudan (TMC) a ranar Lahadi ta musanta duk wani zargin dake nuna cewa ta gabatar da wata bukatar kafa majalisar gudanar da mulki ta hadin gwiwa a kasar.

"Har zuwa wannan lokacin, ba mu samu wasu rubutattun bayanai daga tawagogin masu shiga tsakani ba kuma ba mu yi wata tattaunawa game da batun yin wakilci a majalisar shugabancin kasar ba," Shams-Eddin Kabashi, kakakin majalisar ta TMC, shi ne ya bayyana hakan a taron manema labarai.

Ya kara da cewa, TMC tana sa ran za ta kammala yin nazari kan bayanan da kungiyoyin 'yan hamayya suka gabatar, yana mai cewa ana sa ran za'a karbi martanin da TMC ta gabatar a ranar Litinin.

Ya kuma bayyana kyakkyawar fatar samun nasara a tattaunawar mika shugabancin kasar da ake gudanarwa, yana mai cewa, "babu wata babbar matsalar dake kawo cikas, kuma muna da kyakkyawan yakinin za mu samu nasarar cimma matsayar warware matsalar cikin hanzari a bisa irin cigaban da muka samu a tsakanin bangarorin biyu." (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China