in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta samar da kudaden kara horas da ma'aikata sana'o'in hannu
2019-05-01 15:18:21 cri
Kasar Sin tana shirin samar da kudaden da yawansu zai kai Yuan biliyan 100 kwantankwacin dalar Amurka biliyan 14.8 daga ragowar kudaden asusun inshoran marasa aikin yi na kasar don kara horas da ma'aikata.

Yayin taron majalisar gudanarwar kasar da firaministan kasar Li Keqiang ya jagoranta a jiya Talata, an yanke shawarar cewa, za a samar da wani asusu na musamman domin aiwatar da shirin horas da sana'o'in hannun.

Taron ya kuma bayyana cewa, za a sanar da jama'a kan yadda aka yi amfani da kudade da ma sauran muhimman bayanai kan wannan shiri, a hannu guda kuma za a hukunta wadanda suka yi karyar shiga wannan horo domin su samu kudi kamar yadda doka ta tanada.

Bugu da kari, za a taimakawa manufofin kananan hukumomi game da tallafin samun horon, kana ma'aikatan da suka cancanta za su iya shiga shirye-shiryen samun horo su kuma karbi tallafi.

Taron ya kuma jaddada cewa, wajibi ne a mayar da hankali ga ingancin horon, da kara daga matsayin shiryen-shiryen koyar da sana'o'in. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China