in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
UNICEF ya koka da karuwar rufe makarantu da take hakkokin yara a Mali
2019-04-27 16:47:31 cri

Asusun kula da kananan yara na MDD UNICEF, ya ce damuwarsa na karuwa game da yawan take hakkokin yara a Mali, kamar kisan yara 46 a ranar 23 ga watan Maris a garin Bankass, tare kuma da rufe makarantu.

Kakakin UNICEF Christophe Boulierac ya bayyanawa MDD a Geneva cewa, tabarbarewar yanayin jin kai a Mopti dake yankin tsakiyar Mali saboda rikicin kabilanci da kasancewar kungiyoyi masu dauke da makamai na kara shafar yara masu rauni.

Ya ce, kusa 1 bisa 3n dukkan makarantun yankin Mopti a rufe suke yanzu saboda rashin tsaro, al'amarin dake barazana ga hakkin ilimin yara sama da 157,000 daga cikin yara 260,000 da rufe makarantu a kasar ya shafa.

UNICEF na aiki kafada da kafada da jami'an ba da ilimi a yankunan dake fama da rikici da ma'aikatar ilimi ta kasar, da nufin samar da ilimi mai dorewa ga wadancan yara ta hanyoyin dabaru na wuci gadi kamar koyarwa a cibiyoyin koyo na unguwanni. (Fa'iza Msutapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China