in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta goyi bayan baiwa kasashe masu tasowa kula ta musamman a WTO
2019-04-05 16:03:05 cri
Ma'aikatar cinikayyar kasar Sin ta bayyana cewa, wajibi ne a kiyaye manufa da tsarin baiwa kasashe masu tasowa kula ta musamman(SDT) a kungiyar cinikayya ta duniya(WTO).

Mai magana da yawun ma'aikatar Gao Feng, wanda ya bayyana hakan jiya Alhamis, ya ce, tsarin ya kunshi, sanya tsarin cudanyar kasashen duniya a harkokin cinikayya, kana ko wace mamban kungiyar tana da 'yancin zabar manufofi cinikayya da tattalin arzikin ketare da ya dace da ita.

Yarjeniyar kungiyar WTO ta kunshi tanade-tanaden tsarin na SDT, wanda ya baiwa kasashe masu tasowa 'yanci na musamman, misali, za su iya alkawarin cimma daidaito kan rage haraji maimakon kasashen da suka ci gaba wajen sasantawa a fannin cinikayya.

Da yake karin haske kan yadda kasashe masu tasowa suka amince su janye 'yancinsu na SDT a sasantawa a WTO, Gao, ya ce, kasar Sin, babbar kasa ce mai tasowa, kuma a shirye take ta sauke nauyin dake kanta daidai da matsayi da kuma karfin ci gabanta.

Ya ce, kasar Sin za ta hada kai da sauran kasashe masu tasowa, wajen kare 'yancinsu. Kana a nasu bangare kuma, ya kamata dukkan mambobin WTO, su martaba juna su kuma yi kokarin ganin an yiwa kungiyar gyaran fuska, bisa tsarin cudanyar kasashen duniya.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China