Yau Jumma'a 22 ga wata Geng Shuang, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ya ce, kasar Sin ba ta amince kasar Amurka ta sayar wa Taiwan makamai ba, kuma ba za ta sauya matsayinta kan wannan batu ba. Haka kuma ta riga ta tuntubi Amurka a hukumance.
Rahotanni na cewa, a kwanakin baya ne, gwamnatin Amurka ta kuduri aniyar sayar wa yankin Taiwan jiragen saman yaki kirar F-16 fiye da 60. (Tasallah Yuan)