in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta mayar da hankali kan saukaka fatara ga mutanen dake cikin tsananin bukata
2019-02-24 15:27:09 cri

Gwamnatin kasar Sin ta dauki kwararan matakai a shekarar 2018 wajen tabbatar da kyautata yanayin zaman rayuwar al'ummar kasar masara galihu wadanda ke rayuwa cikin yanayin talauci, kamar yadda ma'aikatar kula da walwalar jama'a ta kasar ta bayyana. Ma'aikatar ta kashe kudade kimanin yuan biliyan 2.25 kwatankwacin dalar Amurka miliyan 335 wajen gudanar da muhimman ayyukan kyautata jin dadin rayuwar jama'a a wasu larduna 22 mafiya fama da talauci a kasar, wanda jimillar ya tasama kashi 80 bisa 100 na adadin kudin da kasar Sin ta kashe wajen gudanar da ayyukan yaki da fatara a shekarar 2018, in ji ma'aikatar.

Ma'aikatar dai ta kyautata rayuwar mutanen dake cikin matsanancin yanayi na bukata, da kuma masu bukata ta musamman ta hanyar ba su kudaden alawus domin kula da rayuwar iyalansu.

Ya zuwa yanzu, mafi karanci kudaden alawus da ake bayarwa a kasar ya wuce matakin da hukumar yaki da fatara ta kasar ta tsara tun da farko. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China