Wannan mataki ya biyo bayan wani muhimmin taro ne da al-Bashir ya gudanar a ranar Juma'a, tare da mambobin kwamitin dake jagorancin tattaunawar kasar, da gwamnonin jahohi da manyan shugabannin jam'iyyar dake mulkin kasar.
Al-Bashir ya ce, sabuwar majalisar ministocin kasar za ta dauki kwararan matakai kan tattalin arzikin kasar, ya kara da cewa, ya umarci kwamitin kolin dake tafiyar da harkokin mulkin kasar da ya ci gaba da tattaunawa har a cimma gaci wajen warware tarzomar kasar. (Ahmad Fagam)