in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamaru za ta sanya harsunan kasar cikin manhajar karatu
2019-02-22 10:41:06 cri
Nan bada dadewa ba, kasar Kamaru za ta sanya harsunan kasar cikin manhajjar karatu a hukumance, a wani bangare na yunkurin kasar na inganta hadin kai tsakanin al'ummominta.

Ministan kula da ilimi a matakin farko na kasar, Laurent Serge Etoundi Ngoa ne ya bayyana haka jiya a birnin Yaounde, yayin bikin ranar Harshen Uwa ta duniya.

Ya ce yanzu matakin ya zama tsari a hukumance, domin kasar ta na son a fara amfani da harsunan a dukkan makarantu.

Kamaru na da harsunan kabilu 260, amma Faransanci da da Ingilishi ne kadai harsunan da take amfani da su a hukumance.

Ministan ya ce manufar sabon matakin ita ce, mayar da harsunan kasar matsayin wadanda da za a rika amfani da su a hukumance a hankali. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China