in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Har yanzu dalibai 170 da malamansu na hannun wadanda suka yi garkuwa da su a kasar Kamaru
2019-02-18 10:13:55 cri
Dalibai akalla 170 da malamansu ne har yanzu ke hannun 'yan bindigar da suka yi garkuwa da su, bayan wasu rahotanni da safiyar jiya na cewa an sake su.

Rev. Oliver Shey, babban jam'in gudanarwa na Kwalejin St. Augustine, ya ce 'yan bindigar sun je makarantar domin mika musu yaran, amma bayan sun lura da suka yi da kasancewar jami'an tsaro a makarantar, sai suka gaggauta dauke yaran tare da tafiya da su maboyarsu.

Kwalejin St Augustine, makarantar sakandare ce ta darikar Katolika dake garin Kumbo na yankin arewa maso yammacin Kamaru, daya daga cikin yankunan kasar 2, dake da rinjayen masu amfani da harshen Ingilishi, wadanda ke fama da rikici.

Rev. Oliver Shey ya ce sun bukaci sojojin su bar harabar makarantar domin ba 'yan bindigar damar dawo da daliban.

Ya ce maimakon dalibai 145 da suka sace ranar Asabar, 'yan bindigar sun shaida musu cewa yanzu suna tare da dalibai 200 kuma 170 daga cikinsu, daliban makarantar ne.

Har ila yau, ya ce dukka daliban da aka sace 'yan mata ne, sai kuma shugaban makarantar da masu gadi biyu da wani malami da iyalansa. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China