in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamfanin kasar Sin zai kafa cibiyoyin wankin koda a kasashen yammacin Afrika
2019-02-22 10:13:44 cri
Wani babban kamfanin zuba jari na kasar Sin, zai fara shirye-shiryen kafa cibiyoyin wankin koda a wasu kasashen yammacin Afrika a cikin wata mai zuwa.

Jian Weihong, mataimakiyar shugaban kamfanin zuba jari a kasashen dake cikin shawarar Ziri Daya da Hanya Daya wato China Silk Road Development Capital Management Company LTD, ta shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, manufar kamfaninsu ita ce, taimakawa wajen inganta harkokin kiwon lafiya.

Jian Weihong, ta sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna da wakilan kasashen da za su ci gajiya aikin a jiya Laraba, yayin bikin bude taron yini 3 kan kiwon lafiya a yankin yammacin Afrika, wanda ke gudana a birnin Accran Ghana. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China