A ranar 27 ga watan nan ne, ake sa ran za a yi taron ministocin harkokin wajen kasashen Sin, Rasha da Indiya karo na 16 a garin Wuzhen dake lardin Zhejiang na kasar Sin.
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang wanda ya sanar da hakan a yau, ya ce mamba a majalisar gudanarwar kasar kana ministan harkokin wajen kasar Wang Yi ne zai jagoranci taron. Ana kuma sa ran ministan harkokin wajen Rasha Sergei Lavrov da takwaransa na kasar Indiya Sushma Swaraj za su halarci taron. (Ibrahim)