Yayin taron ganawa da manema labarai da aka saba yi a nan birnin Beijing, a yau Talata kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta bayyana cewa, kasarta tana fatan yin hadin gwiwa cikin dogon lokaci bisa manyan tsare-tsare da kasar ta Rasha, domin samun moriyar juna.
An ce, a kwanakin baya bayan nan, shugaban kasar Rasha Putin, ya bayyanawa mahalarta dandalin tattalin arzikin kasa da kasa da aka shirya a birnin Saint Peterburg na kasarsa cewa, kasar Sin aminiyar Rasha ce kuma abar dogaro. Ya ce kudurori daban daban da aka tsayar yayin babban taron JKS karo na 19, sun samar da sharudda masu inganci, wajen kara zurfafa huldar dake tsakanin Sin da Rasha. (Jamila)