in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta ce an kwashe bakin haure 159 daga Libya zuwa Nijer
2019-02-15 11:07:45 cri

Ofishin babban kwamishina mai kula da 'yan gudun hijira na MDD (UNHCR) ya sanar a jiya Alhamis cewa, a daren Larabar da ta gabata an kwashe bakin haure kimanin 159 daga kasar Libya zuwa kasar Nijer.

"Bayan tsarewar da aka yi musu na watanni masu yawa a Libya, a daren jiya, wadansu matasa 'yan kasar Eritrea dake neman mafaka, an kwashe su a jirgin sama a karon farko, inda aka sauke su a jamhuriyar Nijer," in ji hukumar ta UNHCR.

An kwashe masu neman mafakar ne daga sashen da hukumar ke tattara su a birnin Tripoli tun a farkon wannan watan, inda ake samar musu da abinci, muhalli mai tsafta, kiwon lafiya, da gyaran tunaninsu, in ji sanarwar.

Kimanin bakin haure 3,175 aka kwashe su daga Libya zuwa Nijer, Italy da Romania, a cewar hukumar MDDr.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China