190201-xi-1.mp4
|
Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya ziyarci gidajen wasu mazauna birnin Beijing, a yau Jumma'a, inda ya taya su, gami da daukacin jama'ar kasar Sin murnar bikin sabuwar shekara bisa kalandar gargajiyar kasar Sin, wanda za a fara a Talata mai zuwa.
Shugaban ya ce, "Ina fatan jama'ar kasarmu za su kara jin dadin zaman rayuwa, haka kuma ina fatan ganin kasarmu ta kara samun ci gaban tattalin arziki da walwala. A karshe ina tare da fata, na ganin an samu jituwa a gidajenku, da ci gaban harkokinku na yau da kullum, sa'an nan ku samu jin dadi da murna a lokacin bikin bazara!" (Bello Wang)