in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta bukaci Amurka ta amince tare da yi wa ci gaban fasahar sauran kasashe adalci
2019-02-01 11:47:43 cri
Ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, ta yi kira ga Amurka, ta amince tare da yi wa nasara da ci gaban fasahar sauran kasashe adalci.

Yayin taron manema labarai da aka saba yi a kullum, kakakin ma'aikatar Geng Shuang, ya ce Amurka ce ke kan gaba ta fannin karfin fasaha a duniya, sai dai bai kamata kasar ta mayar da hankali ga ci gabanta kadai ta hanawa ci gaban sauran kasashe ba.

Wannan tsokaci na zuwa ne bayan mataimakin shugaban kwamitin tattara bayanan sirri na majalisar dattawan kasar Amurka, Mark Warner da shugaban marasa rinjaye na majalisar, Charles Schumer, suka zargi Sin da saci fasahar kasarsu.

Har ila yau, Geng Shuang, ya ce bai dace Amurka ta rika suka da zargin ci gaban fasahar sauran kasashe ba. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China