in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya gana da shugaban IOC
2019-01-31 20:57:45 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da shugaban kwamitin Olympics na kasa da kasa IOC Thomas Bach a yau Alhamis a birnin Beijing na kasar Sin.

Yayin ganawar, shugaba Xi ya ce kasar Sin tana dora cikakken muhimmanci kan aikin karbar bakuncin gasar Olympics ta lokacin sanyi ta shekarar 2022 a birnin Beijing. A cewar shugaban, daukacin jama'ar kasar Sin za su yi kokarinsu, don shirya wata gasar Olympics irin ta kare muhalli, wadda za ta amfani kowa, ta bude kofa domin kowa ya halarta, wadda kuma za ta zama mai tsabta, wato ba tare da aikata zamba a cikin ta ba.

A nasa bangaren, Tomas Bach ya ce, yana da imanin cewa, kasar Sin za ta iya karbar bakuncin gasar Olympics mai kayatarwa. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China