A yau Juma'a, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya jaddada bukatar hade ci gaban fannonin yada bayanai. Shugaba Xi wanda kuma shi ne babban sakataren kwamitin koli na JKS, ya nanata bukatar kara azama wajen bunkasa ayyukan yada aki'dun kasa na tushe tsakanin mambobin jam'iyya, da kuma daukacin al'umma, ta yadda sassan al'ummun kasar za su hade wuri guda, su kuma yi aiki tare cikin himma da kwazo.
Shugaba Xi ya yi wannan tsokaci ne, yayin zaman nazari na jami'an JKS, wanda hukumar siyasa ta kwamitin kolin JKS ta shirya.(Saminu)