in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi ya ba da umarnin daukar matakan tabbatar da adalci don kyautata rayuwar al'umma
2019-01-17 09:52:28 cri

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya bada umarnin ci gaba da kokarin daukar matakan inganta tsarin shugabanci, da gudanar da sauye-sauye, da kuma kafa ingantaccen tsarin siyasa da harkokin shari'a a kasar.

Xi, wanda shi ne babban sakataren kwamitin tsakiyar jamiyyar kwaminis (CPC) ta kasar Sin, kana shugaban kwamitin tsakiyar rundunar sojojin kasar, ya bada umarnin ne a cikin wani jawabin da ya gabatar a babban taron kwamitocin siyasa da na shari'a wanda aka gudanar a birnin Beijing a ranakun Talata da Laraba.

Ya umarci hukumomin tabbatar da doka da na shari'a da su kara kaimi, su daidaita ayyukansu kana su inganta kwarewar aikinsu. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China