in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Guterres ya nada Xia Huang da ya zama manzon musammansa kan batun yankin manyan tafkunan Afirka
2019-01-23 20:09:38 cri

Babban sakataren MDD Antonio Guterres ya nada Xia Huang, tsohon jakadan kasar Sin dake wakilci a kasar jamhuriyar Congo a matsayin manzon sa na musamman kan batun yankin manyan tafkunan Afirka.

A Larabar nan, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta yi maraba da nadin, ta kuma jaddada cewa, Xia Huang zai yi kokari matuka a aikin ingiza zaman lafiya da kwanciyar hankali, da kuma ci gaba a yankin manyan tafkunan Afirka karkashin goyon bayan MDD, kuma ita ma kasar Sin, za ta ci gaba da goyon bayan kokarin babban sakataren MDD da kuma jakadan Xia. (Jamila)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China