in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban AU ya yi Allah wadai da harin da aka kai masu kiyaye zaman lafiya a Mali
2019-01-23 09:56:33 cri
A jiya Talata, shugaban hukumar gudanarwar kungiyar tarayyar Afirka (AU), Moussa Faki Mahamat, ya yi Allah wadai da kakkausar murya kan wani harin da aka kaddamar a kasar Mali, harin da ya kashe sojojin kasar Chadi 10 dake aikin kiyaye zaman lafiya karkashin tawagar MINUSMA ta MDD.

Harin wanda ya abku a ranar Lahadin da ta gabata, a garin Aguelhok dake yankin Kidal na kasar Mali, ya kuma jikkata a kalla wasu 25.

Bayan da sakon ta'aziya da ya aikewa gwamnatin Chadi da iyalan wadanda suka rasa rayuka, shugaban hukumar gudanarwar ta AU ya bukaci hukumomin kasar Mali da kungiyoyin 'yan tawaye da suka sa hannu kan yarjejeniyar tsagaita bude wuta na kasar, da su yi kokarin zakulo wadanda suka aikata wannan mummunan aiki don su girbi abin da suka shuka.

Faki ya bayyana fatansa na ganin wadanda suka ji rauni sun samu sauki cikin sauri, Ya kuma gode musu a madadin daukacin jama'ar nahiyar Afirka a bisa jaruntan da suka nuna. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China