Jiya Laraba ma'aikatar tsaron kasar Nijar ta fitar da wata sanarwa, inda aka bayyana cewa, kwanan baya sojojin kasar sun kaddamar da hari a yankin tafkin Chadi dake kudu maso gabashin kasar, inda sun harbe mayakan kungiyar Boko Haram da yawansu ya kai 287 har lahira.
Sanarwar ta ce, tun daga ranar 28 ga watan Disamban shekarar 2018 zuwa 2 ga wannan wata, sojojin sama da na kasa na kasar Najir sun kaddamar da hare-hare inda suka hallaka mayakan Boko Haram guda 287, tare kuma da karbe makamai da dama daga wajensu, kawo yanzu babu sojojin Nijar da suka rasa rayuka ko jikkata
A cikin sanarwar, rundunar sojojin Nijar ta nuna gamsuwa kan sakamakon da ta samu, kuma ta bayyana cewa, matakan da sojojin kasar suka dauka sun gurgunta kungiyar ta Boko Haram sosai.(Jamila)