Yau Laraba kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang ya bayyana a yayin taron ganawa da manema labaran da aka saba yi a nan birnin Beijing cewa, batun Taiwan harkar ce ta cikin gida na kasar Sin, kana batu ne da ya shafi babbar moriyar kasar Sin da yadda al'umma ke kishin kasar, bai kamata kasashen waje su tsoma baki a ciki ba, a don haka kasar Sin ta bukaci Amurka da ta nace ga manufar kasar Sin daya kacal a duniya da manufofin da aka tsara a cikin hadaddun sanarwa guda uku da kasashen Sin da Amurka suka fitar cikin hadin gwiwa, haka kuma ta daidaita batun Taiwan ta hanyar da da ta dace.(Jamila)