in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta yi Allah wadai da zargin da Amurka ta yi mata kan batun satar bayanai ta intanet
2018-12-21 15:00:14 cri

Gwamnatin kasar Sin ta yi Allah wadai da zargin da kasar Amurka ta yi mata game da batun tsaron intanet da kuma gurfanar da wasu Sinawa biyu bisa zarginsu da laifin satar bayanai ta intanet, kakakin ma'aikaar harkokin wajen kasar ne ta bayyana hakan a yau Juma'a.

Wata sanarwa da kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta fitar, ta ce, zargin da Amurkar ta yi ba shi da tushe balle makama, zargin ya saba da muhimman ka'idojin kasa da kasa, kana zai iya lahanta dangantakar dake tsakanin kasashen biyu.

"Kasar Sin ta yi fatali da wannan zargi, kana ta gabatarwa wakilan bangaren Amurka kurafinta kan wannan batu." in ji Hua.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China