in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhu ya bukaci a gudanar da zabe mai adalci a Guinea-Bissau
2018-12-28 09:35:00 cri
Kwamitin sulhun MDD ya bukaci masu ruwa da tsaki a harkokin siyasar kasar Guinea-Bissau, da su nuna halin dattaku da sanin ya kamata ta hanyar gudanar da zabe mai adalci da zai samu karbuwa ga kowa a kasar, har ma ya kai ga wanzuwar zaman lafiya.

Da yake karin haske cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai, kwamitin sulhun ya bayyana damuwa kan yadda aka gaza gudanar da zabuka a ranar 18 ga watan Nuwamba kamar yadda aka shirya. Ya kuma bayyana damuwa matuka game da shirye-shiryen gudanar da zabukan da aka shirya gudanarwa a ranar 10 ga watan Maris na shekarar 2019 dake tafe.

Sanarwar ta ce, shirya zabuka cikin adalci a 'yar karamar kasa dake yammacin Afirka a watan na Maris, zai share turbar wanzar da zaman lafiya a kasar.

Matakin farko na aiwatar da gyare-gyare a kasar, shi ne zabukan 'yan majalisun dokoki , gabanin zaben shugaban kasa da ake fatan shiryawa a shekarar 2019. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China