Sanarwar ta IGAD ta jiyo babban sakataren zartaswar kungiyar IGAD, Mahboub Maalim, yana cewa, "Muna goyon bayan jama'ar kasar Somalia da gwamnatin kasar wajen yin Allah wadai da wannan mummunan aiki na ta'addanci da aka aikata, kana muna jajantawa iyalan wadanda suka rasa rayuka sakamakon harin, tare da fatan wadanda suka jikkata za su warke cikin sauri. "(Bello Wang)