in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masu ruwa da tsaki na kira da a hada gwiwa domin tsagaita wuta a arewacin Somalia
2018-05-25 10:41:07 cri
Abokan huldar kasar Somalia dake tallafawa yakin da kasar ke yi da 'yan ta'adda, sun bayyana damuwa game da sabbin tashe tashen hankula da suka barke tsakanin dakarun yankunan Somaliland da Puntland a wajen garin Tukaraq na yankin Sool.

Wata sanarwar hadin gwiwa da MDD, da kungiyoyin EU, da AU, da ta raya gabashin Afirka ta IGAD, da kuma Amurka da ma wasu sauran kasashe suka fitar, ta yi kira da a gaggauta dakatar da bude wuta, a kuma koma teburin shawarwari.

Sanarwar na zuwa ne, biyowa bayan barkewa tashin hankali a ranar Alhamis, inda sassan biyu suka yi amfani da manyan makamai domin kaiwa juna hari.

Mahukuntan yankunan biyu, sun zargi juna da fara tada rikicin da ya tada hankulan al'umma a yankin na arewacin Somalia. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China