Wasu 'yan bindiga sun hallaka mutane 14, tare da raunata wasu 17, yayin wani farmaki da suka kaddamar kan taron masu bikin aure a kauyen Paa-Gwandara dake karamar hukumar Jema'a a jihar Kadunan Najeriya.
Rahotanni sun bayyana cewa, 'yan bindigar sun kaddamar da harin ne da almurun ranar Lahadi, inda bayan yiwa taron jama'ar tsinke, suka bude wuta, kuma nan take suka hallaka mutane 9, yayin da wasu karin mutane 5 suka rasu a asibiti. Cikin wadanda suka jikkata dai har da yara kanana 6 wadanda a cewar wasu ganau suna ci gaba da samun kulawa jami'an lafiya.
Rundunar 'yan sandan yankin dai ta ce, ta fara gudanar da bincike game da aukuwar wannan lamari, kamar dai yadda shugaban karamar hukumar ta Jema'a Peter Averik ya tabbatar.(Saminu)