in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An tabbatar da mutuwar mutane 4 sanadiyyar cutar zazzabin lassa a Nijeriya
2018-12-12 09:04:22 cri
An tabbatar da mutuwar mutane 4 sanadiyyar barkewar cutar lassa a baya-bayan nan, a jihar Gombe dake arewa maso gabashin Nijeriya.

Mukaddashin babban jami'in dake nazarin yaduwar cutuka a cikin al'umma na jihar, Nuhu Bille, ya shaidawa manema labarai jiya Talata cewa, ana zargin mutane 53 sun kamu da zazzabin tun bayan barkewarsa a jihar cikin watan da ya gabata, inda ya ce mutane 4 sun mutu yayin da suke jinya a asibitin da gwamnati ta kebe.

Bisa kiddigar da aka yi a hukumance, ya ce adadin wadanda suka mutu sanadiyyar cutar ya zama 18, biyo bayan mutuwar ta baya-bayan nan. Ya kara da cewa wasu mutane 546 sun yi jinya sanadiyyar cutar a bana.

A ranar 22 ga watan Nuwamba ne cibiyar takaita yaduwar cutuka ta Nijeriya NCDC, ta ce zazzabin lassa ya yi sanadin mutuwar akalla mutane 143 a fadin kasar. An samu rahoton bullar cutar a jihohi 22 da kananan hukumomi 90, tun bayan da aka gano bullarta a ranar 1 ga watan Junairu.

A cewar hukumar ta NCDC, akalla mutane 3,016 ne ake zargin sun kamu da cutar a bana. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China