Halima Muqaddas, kwaminishar kula da harkokin kiwon lafiya a jihar Bauchi, a jiya Jumma'a, ta bayyanawa wakilin kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, daga karshen watan Janairu zuwa yanzu, mutane biyar ne sun kamu da cutar.
A cewarta, akwai alamar daya daga cikin wadanda suka kamu da cutar na samu sauki.
Nijeriya dai ta umurci asibitocin kasar su kula da wadanda ake hasashen sun kamu da cutar yadda ya kamata, don tabbatar da gane ainihin wadanda suka kamu da cutar cikin sauri.
Gaba daya, mutane 12 ne suka mutu sakamakon yaduwar cutar ta Lassa a Nijeriya tun daga wata Nuwamban bara, a yayin da adadin ya kai sama da 80 tun bayan da cutar ta bulla a farkon shekarar da ta gabata.(Lubabatu)