in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
A Najeriya an sake samun bullar cutar zazzabin Lassa
2016-04-07 09:32:36 cri
Mahukunta a Najeriya sun ce an sake gano bullar zazzabin lassa bayan gudanar da gwaje gwaje kan wani matashi dan shekaru 27 a jahar Katsina dake arewa maso yammacin kasar.

Wannan dai shi ne karo na farko, da aka taba samun rahoton bullar cutar a shiyyar arewa maso yammacin kasar.

Kwamishiniyar lafiya ta jahar Katsina Mariyatu Bala Usman, ta shedawa kamfanin dillancin labaran kasar Sin Xinhua cewar, tuni aka killace matashin tun bayan da aka hakikance yana dauke da kwayoyin lassa mai saurin hallaka bil adama.

A cewar jami'ar lafiyar, ana zargin matashin ya kamu da cutar ne bayan da ya kusanci gawar wani mukarrabinsa.

Mariyatu ta fada cewa, tuni aka ankarar da jami'an kiwon lafiya a dukkan cibiyoyin kiwon kafiya na jihar game da matakan da ya dace su dauka wajen tunkarar bullar cutar a dukkan yankunan kananan hukumomin jihar 34.

Kawo yanzu mutane 268 ne aka zargin sun kamu da cutar zazzabin lassa a fadin kasar, sannan mutane 138 sun mutu tun bayan bullar cutar wacce tafi kamari a watan Fabrairu.

Sai dai mahukunta Najeriya sun tashi haikan domin dakile ci gaba da yaduwar cutar. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China