in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta kara samun ci gaba wajen kiyaye ikon mallakar fasaha
2018-12-08 17:00:52 cri
Kwanan baya, babban alkalin kasar Sin, kuma shugaban kotun jama'a ta koli na kasar Zhou Qiang, ya shugabanci wani taro, inda aka duba da kuma zartas da ka'idojin kotun jama'a ta koli game da batutuwan da suka shafi kotun mallakar fasaha. Wannan kotun ta mallakar fasaha da zata soma aiki, zata kula da shari'o'in da aka daukaka kara game da hakkin kwararrun masu mallakar fasaha a duk fadin kasar.

Manazarta sun nuna cewa, kotun jama'a ta koli ta kafa wannan kotun mallakar fasaha, da kuma daukar nauyin sake yin shari'a kan wasu batutuwan laifi na keta hakkin mallakar fasaha, wannan ya nuna cewa, gwamnatin kasar Sin tana kokarin kyautata tsarin yanke hukunci kan batun laifi na mallakar fasaha, da nufin ingantawa da kiyaye ayyukan yin kirkire-kirkire kan kimiyya da fasaha. Kana ya kara nunawa kasashen duniya aniyar kasar da karfin da ta nuna wajen kara kiyaye mallakar fasaha. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China