in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin: An gudanar da taro domin ranar yaki da cin hanci ta kasa da kasa
2018-12-07 10:10:25 cri
Mahukuntan kasar Sin sun shirya wani kwarya-kwaryar taro, domin maraba da kewayowar ranar kasa da kasa ta yaki da cin hanci da rashawa. Taron dai ya gudana ne a jiya Alhamis, gabanin ranar yaki da rashawa ta kasa da kasa karo na 15, wadda a bana za ta kasance ranar Lahadi 9 ga wata.

Da yake tsokaci yayin taron, mataimakin sakataren hukumar koli ta ladaftarwa da bincike, kuma shugaban babbar hukumar sanya ido ta kasar Sin Yang Xiaodu, ya yi kira da a kara martaba ikon MDD, na taka rawar gani a fannin yaki da cin hanci da rashawa, da hadin gwiwar kasashen duniya a fannin.

Mr. Yang ya ce akwai bukatar zurfafa ayyukan gudanarwa a mataki na jam'iyya mai mulkin kasar Sin, da kara inganta yaki da cin hanci yadda ya kamata.

Babban magatakardar MDD Antonio Guterres, ya aike da rubutaccen sakon fatan alheri ga taron na birnin Beijing, yana mai jaddada kudurin MDD na ci gaba da goyon bayan kasa da kasa a fannin yaki da cin hanci.

Taron dai ya samu halartar wakilai daga kasashe 125, da sauran kungiyoyin kasa da kasa dake aiki a kasar Sin. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China