in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya gana da firaministan kasar Portugal
2018-12-06 10:07:49 cri

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gana da firaministan kasar Portugal, Antonio Costa a jiya Laraba, a Lisbon, fadar mulkin kasar ta Portugal.

A wajen ganawar tasu, shugaban na kasar Sin ya ce bangaren Sin, na son yin kokari tare da Portugal, wajen kara kyautata huldar dake tsakanin kasashen 2, irin ta hadin gwiwa a fannoni daban daban, musamman ma a fannin manyan tsare-tsare.

A nasa bangare, firaministan kasar Portugal Antonio Costa, ya ce kasarsa tana rungumar manufar bude kofa da hadin gwiwa, gami da ciniki cikin 'yanci, sa'an nan kasar tana son halartar shawarar "Ziri daya da Hanya daya" wadda kasar Sin ta gabatar. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China