Ministan lafiya da yaki da cutar kanjamau na kasar Burundi Thaddee Ndikumana ya ce, kasarsa ta shirya tsaf don yiwa 'yan kasar sama da miliyan 7 alluran riga kafin cutar sankarau, kwatankacin kaso 77 cikin 100 da daukacin al'ummar kasar.
Shirin riga kafin wanda zai gudana daga ranar 4 zuwa 13 ga watan Disamba mai kamawa, zai shafi 'yan kasar masu shekara 1 zuwa talatin da haihuwa.
Hukumar lafiya ta duniya WHO ta bayyana cewa, kasar ta Burundi dake yankin tsakiyar Afirka, tana daya daga cikin kasashe 26 na kasashen Afirka dake yankin kudu da hamadar Afirka dake kan gaba wajen fama da wannan cuta.(Ibrahim)