Hukumar lafiya ta duniya WHO ta ce, kimanin ma'aikatan lafiya duba 1 dake yankunan da suka yi hadarin kamuwa da cutar Ebola a kasar Uganda ne aka yiwa alluran riga kafin kamuwa da cutar.
WHO ta kuma bayyana a cikin wata sanarwa cewa, ya zuwa an yiwa ma'aikatan lafiya da ragowar ma'aikatan dake sahun gaba wajen yaki da wannan cuta 1,175 cikin 2,000 da ake fatan yiwa riga kafin kamuwa da cutar a gundomomi biyar dake kan iyaka da Jamhuriyar demokiradiyar Congo(DRC).(Yaya Ibrahim)