A cewar alkaluman kididdiga na baya bayan nan wanda ma'aikatar lafiyar kasar ta wallafa, an samu rahotannin bullar cutar kimanin 200 a yankin Beni da kewaye dake lardin Kivu ta arewa, kuma daga cikinsu, mutane 117 cutar ta hallaka, yayin da mutane 61 da suka kamu da cutar sun riga sun warke.
Bayan taron tattaunawa da aka gudanar a Geneva, hukumar ta WHO ta sanar da cewa, a halin yanzu, cutar Ebola a DRC bata cikin yanayi na mummunar barazana dake bukatar daukin gaggawa daga kasa da kasa.