Rahoton da rundunar 'yan sandan kasar ta wallafa jiya a shafin intanet, ya ce, ana ci gaba da aikin ceto a yankin, sa'an nan, za a gabatar da karin bayani kan batun.
Ya zuwa yanzu, ba a tabbatar da yawan mutanen dake cikin jirgin ruwan a lokacin da hadarin ya auku ba.
Jiragen ruwan Uganda su kan nitse sakamakon daukan mutane fiye da kima da kuma sauran wasu dalilai. Ko a ranar 22 ga watan Maris din shekarar 2014, nitsewar jirgin ruwa a tabkin Albert dake yammacin kasar, ya yi sanadin mutuwar mutane a kalla 108. (Maryam)