in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin zata zamanantar da tsarin kwastam na kasar Uganda
2018-06-28 10:47:40 cri
A jiya Laraba kasashen Uganda da Sin suka rattaba hannu kan wata yarjejeniya inda kasar Sin zata samar da kudaden aikin zamanantar da tsarin gudanarwar hukumar kwastam ta kasar Uganda.

Matia Kasaija, ministan kudi da bunkasa tattalin arzikin kasar ne ya rattaba hannun kan yarjejeniyar a madadin gwamnatin Uganda yace aikin wanda zai lashe kudi kimanin dala miliyan 15 zai taimaka wajen habaka hanyoyin samun kudaden shigar kasar.

Kasaija yace, kasar Sin zata samar da na'urorin bincika jikin dan adam, da tsarin kiyaye hadura a tsarin kwastam na zamani, da abubuwan da zasu tallafawa ayyukan kwastam da dai sauransu.

Yace bayan aiwatar da ayyukan, ba za'a taba samun damar yin fasakwaurin kayayyaki ba akan iyakokin kasar.

Zheng Zhuqiang, jakadan kasar Sin a Uganda wanda ya rattaba hannu a madadin gwamnatin Sin yace, aikin wani bangare ne na tabbatar da nasarorin yarjejeniyar dandalin hadin gwiwar Sin da Afrika.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China