Yau Laraba da yamma, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya komo nan birnin Beijing bayan da ya kammala ziyarar aiki da ya kai kasashe uku wato Papua New Guinea da Brunei da kuma Philippines, kana yayin ziyarar, shugaba Si ya halarci kwarya-kwaryar taron shugabannin kasashe mambobin kungiyar APEC karo na 26 da kuma ganawa da shugabannin kasashen dake tsibirran tekun Pasifik wadanda suka kulla huldar diplomasiyya da kasar Sin.(Jamila)