A yau Talata ne kasashen Sin da Philippines suka daga matsayin alakar dake tsakaninsu zuwa hadin gwiwar manyan tsare-tsare, tare da amincewa su kara gina shawarar ziri daya da hanya daya.
An kai ga cimma wannan matsaya ce, bayan wata ganawa da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi da takwaransa na kasar Philippines Rodrigo Duturte Talatar nan.
Yau da safe ne dai shugaba Xi ya isa Manila, babban birnin kasar ta Philippines, don fara ziyarar aiki ta farko da wani shugaban kasar Sin ya kai kasar cikin shekaru 13. (Ibrahim)