in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta ce bai kamata takunkumai kan Libya su shafi rayuwar fararen hula ba
2018-11-09 10:11:18 cri

Zaunannen wakilin kasar Sin a MDD Ma Zhaoxu, ya ce ya kamata a kaucewa mummunan tasirin takunkumai a kan Libya, sannan bai kamata su shafi rayuwar fararen hula ba.

Ma Zhaoxu, ya shaidawa taron kwamitin sulhu na MDD a jiya cewa, takunkuman ba manufofi ba ne, don haka bai kamata su shiga rayuwar fararen hulan kasar ba.

Kasar Sin ta kuma bukaci kasa da kasa su kara mara baya ga farfadowar doka da oda a Libya, domin samar da maslahar siyasa da za ta kunshi kowa da kowa. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China