Gwamnatin jihar Lagos dake kudancin Nijeriya, ta tabbatar da mutuwar mutane 3, yayin da wasu 5 suka bata, sanadiyyar kifewar kwale-kwale a jihar.
Fasinjoji 20 ne ke cikin kwale-kwalen a lokacin da ya kife da yammacin ranar Laraba, a kusa da tsibirin Tin Can.
Kwale-kwalen ya kife ne mintoci kalilan bayan tashinsa, inda ya nufi garin Ojo dake wajen birnin Lagos.
Babban manajan hukumar ba da agajin gaggawa ta jihar, Adesina Tiamiyu, ya shaidawa manema labarai cewa, an ceto mutane 12, kana ana ci gaba da aikin neman wadanda suka bace.
Ya kara da cewa, tuni aka kaddamar da bincike don gano musababbin hatsarin. (Fa'iza Msutapha)