in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi ya gana da firayin ministan Pakistan
2018-11-02 20:18:46 cri

Yau a nan birnin Beijing shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi ganawa da firayin ministan kasar Pakistan Imran Ahmed Khan Niazi wanda ke yin ziyara a kasar Sin.

Xi ya yi maraba da zuwan Mr. Khan Sin, yana mai bayyana cewa, kasashen Sin da Pakistan aminai ne a ko da yaushe, duk da cewa yanayin da kasashen duniya ke ciki ya samu manyan sauye-sauye, amma huldar dake tsakanin kasashen biyu, ta samu ci gaba yadda ya kamata, kuma tana cike da kuzari. Kaza lika al'ummun kasashen biyu sun samu moriya daga hadin gwiwar dake tsakaninsu, wanda hakan ke sa kaimi ga ci gaban kasashen duniya baki daya.

Xi ya yi nuni da cewa, nan gaba kamata ya yi sassan biyu su kara zurfafa cudanyar dake tsakaninsu, ta yadda za su gudanar da hadin gwiwa a dukkanin fannoni.

A nasa bangare, Imran Khan ya bayyana cewa, kasarsa tana jinjinawa sakamakon da kasar Sin ta samu, tana kuma fatan za ta iya koyi daga fasahohin da kasar Sin ta samu, a fannin raya kasa, da yaki da talauci, da dakile cin hanci da rashawa. Ya ce Pakistan tana son kara zurfafa huldar dake tsakaninta da kasar Sin, domin kara ciyar da tattalin arzikin Pakistan gaba yadda ya kamata.(Jamila)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China