Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya jaddada cikakken goyon bayan gwamnatin sa, da tallafi, da kuma kulawa ga sassa masu zaman kan su, ta yadda za su kara samun ci gaba a dukkanin fannoni.
Shugaban wanda shi ne kuma babban sakataren kwamitin koli na JKS, kana shugaban hukumar zartaswar rundunar sojojin kasar, ya bayyana hakan ne a Alhamis din nan, yayin da yake jagorantar wani taron karawa juna sani, game da batutuwan da suka shafi sassa masu zaman kan su.(Saminu)